Mukhtar Ramalan Yero

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Mukhtar Ramalan Yero
gwamnan jihar Kaduna

15 Disamba 2012 - 29 Mayu 2015
Patrick Ibrahim Yakowa - Nasir Ahmad el-Rufai
Rayuwa
Haihuwa Zariya, 1 Mayu 1968 (55 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Hausawa
Harshen uwa Hausa
Karatu
Makaranta Jami'ar Ahmadu Bello
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa
Imani
Jam'iyar siyasa Peoples Democratic Party

Alhaji Mukhtar Ramalan Yero (An haife shi a ranar 1 ga watan Mayun shekara ta alif ɗari tara sittin da takwas1968A.C) Miladiyya. ɗan siyasan Najeriya ne wanda ya yi Kwamishinan Kudi na Jihar Kaduna daga shekara ta 2007 zuwa watan Mayun shekara ta 2010 lokacin da Patrick Ibrahim Yakowa ya sanya shi a matsayin Mataimakin Gwamna bayan ya gaji Namadi Sambo wanda ya zama Mataimakin Shugaban Najeriya. A watan Disamban shekara ta 2012, ya zama Gwamnan Jihar Kaduna bayan mutuwar Patrick Ibrahim Yakowa a cikin haɗarin jirgin sama mai saukar ungulu yero an nadashi a matsayin dallatun zazzau daga masarautar zazzau ta Zaria a lokacin da ya zama gwamnan jihar.[1][2][3]

farkon rayuwar sa[gyara sashe | gyara masomin]

An haife shi a cikin garin Zaria a ranar 1 ga watan mayun shekara 1968 a kaura a cikin garin Zaria.

Aure[gyara sashe | gyara masomin]

dallatun zazzau Yana da matar aure Mai suna Fatima suna da Yara guda shida.

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Yayi karatun firamare a LEA primary school kaura daga shekarar 1974 zuwa 1980,daga Nan yayi karatun sakandiri a secondary school ikara day da kuma secondary school Zaria mukhtar ya fara karatun difloma a bangaren banking a shekarar 1988 , sannan Kuma yayi karatun a bangaren accounting a 1991, ya Kuma yo karatun masters in business administration a 2003, yayi bautan kasa a jihar Ogun, yayi aiki a banki me zaman kamshi a wurare da dama.

[4]7.

Harkar siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Bayan zaben Alhaji Namadi Sambo a shekara ta 2007, an nada shi a matsayin Kwamishinan Kudi daga shekara ta 2007 zuwa Mayun shekara ta 2010. Gwamna Patrick Ibrahim Yakowa ne ya zabe shi domin cike gurbin kujerar Mataimakin Gwamnan a shekara ta 2010. A watan Disambar shekara ta 2012, ya zama Gwamnan jihar Kaduna bayan mutuwar Patrick Ibrahim Yakowa a wani hatsarin jirgin sama mai saukar ungulu a jihar Bayelsa.

A watan Afrilu na shekara ta 2015, bai yi nasarar sake tsayawa takara ba a hannun abokin hamayyarsa Nasir Ahmad el-Rufai na All Progressive Congress .

Duba kuma[gyara sashe | gyara masomin]

  • Jerin sunayen gwamnonin jihar Kaduna

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

 

  1. "Nigeria air crash kills Kaduna governor Patrick Yakowa". BBC News.Com. 15 December 2012. Retrieved 26 September 2021.
  2. "Gawar Patrick Yakowa ta isa Kaduna". BBC Hausa.Com. 18 December 2018. Retrieved 26 September 2021.
  3. "An rantsar da sabon gwamna a Kaduna". DW.hausa.com. 16 December 2012. Retrieved 27 September 2021.
  4. https://saharareporters.com/2012/12/15/mukhtar-ramalan-yero-become-kaduna-state-governor