Baba Gana Kingibe

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
Baba Gana Kingibe
Secretary to the Government of the Federation (en) Fassara

29 Mayu 2007 - 8 Oktoba 2008
Ministan harkan kasan waje

1993 - 1995
Matiyu Mbu - Tom Ikimi (en) Fassara
Minister of Interior (en) Fassara

Rayuwa
Haihuwa Jihar Borno, 25 ga Yuni, 1945 (78 shekaru)
ƙasa Najeriya
Ƙabila Hausawa
Harshen uwa Hausa
Mutuwa University of Sussex (en) Fassara
Karatu
Harsuna Turanci
Hausa
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a Mai wanzar da zaman lafiya

Baba Gana Kingibe (An haife shi ranar 25 ga watan Yunin,a shekara ta alif dari tara da arba'in da biyar1945) Miladiyya. a jahar borno.

Farkon rayuwa da Karatu[gyara sashe | gyara masomin]

Kingibe an haife shi a jihar borno da tarayyar Najeriya. yayi makarantar firamare a Maiduguri babban birnin jihar.

A shekara ta 1958, ya samu gurbin shiga makarantar sakandare ta lardin Borno.[1] A shekara ta 1960, ya tafi ƙasar Ingila don samun tallafin gwamnati don kammala karatunsa na sakandire a Kwalejin Bishop's Stortford.

A shekara ta 1968, ya sami digirinsa na farko a fannin hulda da kasashen duniya daga Jami'ar Sussex (tare da Thabo Mbeki) kafin ya wuce makarantar BBC television training school da ke Landan. Daga baya Kingibe ya halarci Graduate international studies Gene.

Aiki[gyara sashe | gyara masomin]

Ya fara aiki a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya. kuma ya zama shugaban sashen kula da harkokin yau da kullum a gidan rediyon Arewacin Najeriya (BCNN).

A shekara ta 1972, ya shiga aikin ma'aikatar harkokin wajen Najeriya inda ya fara aikinsa a matsayin babban mai ba da shawara kan harkokin siyasa daga bisani ya zama shugaban hukumar kula da harkokin siyasa.

A shekarar 1981, aka nada shi jakadan Najeriya a Girka da Cyrus. Daga baya Janar Ibrahim Babangida ya nada Kingibe Jakadan Najeriya a Pakistan. kuma yayi aiki daga watan Oktoba a shekara ta (2002 zuwa watan Satumba a shekara ta 2006), a matsayin special envoy of the African union a Sudan sannan kuma wakilin musamman na shugaban hukumar Tarayyar Afirka da kuma shugaban tawagar Tarayyar Afirka a Sudan.[2]

Bayan yunkurin juyin mulkin da Najeriya ta yi a shekara ta ( 1976), Kingibe ya zama babban sakataren harkokin siyasa, daga shekara ta(1976 zuwa shekara ta 1979), inda ya shiga cikin shirin mika mulki na sojoji, a jihohin. ƙirƙira da ƙayyadaddun ƙasa, gyare-gyaren ƙananan hukumomi da kwamitin tsara tsarin mulki na Jamhuriyar Najeriya ta biyu. Wannan matsayi ya kasance a lokaci guda a matsayin babban sakataren siyasa a ofishin shugaban kasa tsakanin shekara ta (1976 zuwa shekara ta1981), inda yayi hidima ga Janar Olusegun Obasanjo da shugaban kasa Shehu Shagari. Daga baya Kingibe ya zama babban sakatare mai kula da ayyuka na musamman a cikin ofishin majalisar ministocin, tsakanin shekara ta( 1981 zuwa shekara ta 1984).[3]

Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Siyasar jam'iyya[gyara sashe | gyara masomin]

Kingibe ya shiga siyasar jam’iyya ne a cigaba da neman sauyi a jamhuriya ta uku a Najeriya. A shekara ta (1988), aka naɗa shi daraktan kungiyar ‘yan adawa ta Najeriya wanda ya kunshi ‘yan siyasa irin su Atiku Abubakar, Bola Tinubu, Abdullahi Aliyu Sumaila da Rabiu Kwankwaso wanda Shehu Musa Yar'Adua ya jagoranta a lokacin.

Daga baya ya shiga jam'iyyar Social Democratic Party a shekara ta (1989), A lokacin da aka gudanar da zabubbukan mukaman zartarwa na kasa (Na jam'iyyar SDP) bangaren jam'iyyar SDP ne suka dauki nauyin Kingibe a matsayin shugaban jam'iyyar, inda ya ci gaba da rikewa. A matsayinsa na shugaban jam'iyyar, Kingibe ya taka rawa wajen shirya zaben fidda gwani na gwamnoni da na shugaban kasa a shekarar 1991 da 1992.

A shekarata 1999 Shehu Musa Yar'Adua ya tsaya takara, Shima Kingibe ya gabatar da kansa a matsayin dan takarar shugaban kasa. Ya raba gari da kungiyarsa ta PFN inda ya yi amfani da dangantakarsa da shugabannin jam’iyyar SDP na jihar wajen gina yakin neman zabensa. Ya sha kaye a zaben fidda gwani da aka gudanar a Jos amma bayan da Gwamnonin SDP suka nuna masa, sai MKO Abiola da ya lashe zaben fidda gwani ya zabe shi a matsayin mataimakin shugaban kasa , inda ya samar da tikitin tsayawa takarar Musulmi da Musulmi wanda tun da farko ake tunanin zai kawo cikas ga yarjejeniyar. A shekara ta 1993 ), ya zama dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam'iyyar Social Democratic Party.[4]

Zaben shugaban kasa na 1993[gyara sashe | gyara masomin]

MKO Abiola ne samu rinjayen kuri'u duk da cewa an soke sakamakon zaben da Janar Ibrahim Babangida yayi.

Bayan soke zaben shugaban kasa, yazama jami'in diflomasiyya wanda ya yi ministan harkokin waje A Gwamnatin Sani Abacha a matsayin Ministan Harkokin Waje daga shekara ta(1993 zuwa shekara ta1995), Ministan Harkokin Cikin Gida daga shekara ta( 1995 zuwa shekara ta 1997), da Ministan Wutar Lantarki da Karfe daga shekara ta(1997 zuwa shekara ta1998), [5]

A watan Satumban (2006), Kingibe ya dawo Najeriya ana kyautata zaton Kingibe ya yi tunanin tsayawa takarar shugaban kasa , kafin daga bisani ya koma gwamnatin Yar'adua. ya koma jam'iyyar PDP gabannin zaben shugaban kasa na shekara ta (2007 ), wanda Umaru Musa Yar'Adua ya lashe. A watan Yuni shekara ta( 2007),[6] Shugaba Umaru 'Yar Adua ne ya nada shi sakataren gwamnatin tarayya . kuma shine ya tsige shi a ranar (8), ga watan Satumba a shekara ta ( 2008), bayan yada jita-jita game da rashin lafiyar sa.

Gwamnatin Buhari[gyara sashe | gyara masomin]

Shugaba Muhammadu Buhari Ya nada Kingibe mamba a kwamitin rantsar da Buhari Tun daga wannan lokacin, ya ci gaba da yin aiki tare da Abba Kyari a matsayin mai karfi Fada aji na gwamnatin Buhari a bayan fage ana alakanta shi da hukumomin leken asiri da manufofin kasashen waje. A watan Yuni shekara ta (2018), Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da ranar( 12), ga watan Yuni a matsayin ranar Dimokradiyya kuma ya ba Kingibe lambar yabo a wannan rana.

A ranar( 31) ga watan mayu a shekara ta (2021), Buhari ya nada Kingibe a matsayin Jakade na musamman a kasar Chadi, yankin tafkin.

Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]