Misra
|
جُمهورِيّةُ مِصرَ العَرَبيّةِ (ar) مصر (ar) Arab Republic of Egypt (en) Egypt (en) Republik Arab Mesir (ms) Mesir (ms) | |||||
|
|||||
|
| |||||
|
| |||||
| Take |
Bilady, Bilady, Bilady (en) | ||||
|
| |||||
|
| |||||
| Kirari | «مصر أمّ الدنيا» | ||||
| Suna saboda |
Ptah (en) | ||||
| Wuri | |||||
| |||||
| Babban birni | Kairo | ||||
| Yawan mutane | |||||
| Faɗi | 114,535,772 (2023) | ||||
| • Yawan mutane | 113.36 mazaunan/km² | ||||
| Harshen gwamnati | Larabci | ||||
| Labarin ƙasa | |||||
| Bangare na | Arewacin Afirka, Gabas ta tsakiya da Yammacin Asiya | ||||
| Yawan fili | 1,010,407.87 km² | ||||
| Wuri a ina ko kusa da wace teku | Bahar Rum, Nil da Red Sea | ||||
| Wuri mafi tsayi |
Mount Catherine (en) | ||||
| Wuri mafi ƙasa |
Qattara Depression (en) | ||||
| Sun raba iyaka da | |||||
| Bayanan tarihi | |||||
| Mabiyi |
Kingdom of Egypt (en) | ||||
| Ƙirƙira |
28 ga Faburairu, 1922: Kingdom of Egypt (en) | ||||
| Tsarin Siyasa | |||||
| Tsarin gwamnati | jamhuriya | ||||
| Majalisar zartarwa |
Cabinet of Egypt (en) | ||||
| Gangar majalisa |
Parliament of Egypt (en) | ||||
| • Shugaban kasar Egypt | Abdul Fatah el-Sisi (8 ga Yuni, 2014) | ||||
| • Prime Minister of Egypt (en) |
Mostafa Madbouly (en) | ||||
| Majalisar shariar ƙoli |
Supreme Constitutional Court of Egypt (en) | ||||
| Ikonomi | |||||
| Nominal GDP (en) | 424,671,765,456 $ (2021) | ||||
| Kuɗi | Fam na Masar | ||||
| Bayanan Tuntuɓa | |||||
| Kasancewa a yanki na lokaci | |||||
| Suna ta yanar gizo |
.eg (mul) | ||||
| Tsarin lamba ta kiran tarho | +20 | ||||
| Lambar taimakon gaggawa |
122 (en) | ||||
| Lambar ƙasa | EG | ||||



Ƙasar Misra, ko Masar tana kudu maso, gabashin Afrika, kuma tana kudu maso yammacin Asiya [1] ɗaya daga cikin muhimman siffofin da take taƙama da su shi ne na kasancewa ta a kan mararraba, ta kusa da nahiyar Turai. Sannan kuma tana matsayin ƙasar da ta kasance mashiga tsakanin Afirka da nahiyar Asiya. Har ila yau kuma, ita ce kuma ta haɗa hanyar safara ta cikin ruwa, tsakanin tekun Mediterrenean da tekun Indiya ta hanyar Bahar Maliya.

Dalar Giza da ke birnin Al-ƙahirar Kasar. Misra ko ƙasar Masar dai ta kasance ƙasa mafi yawan al'umma a cikin dukkanin ƙasashen Larabawa, kuma babban birninta wato birnin Al'ƙahira shi ne birni mafi girma a nahiyar Afirka tun ƙarnoni da dama da suka gabata. Sannan kuma har ila yau, ga ta a ƙarshen kogin nilu, wanda shi ne kogi mafi girma a duniya. Saboda haka, idan aka yi la'akari da waɗannan dalilai na tarihi, to za a iya fahimtar dalilin da ya sa matsayin ƙasar Misra yake da ƴar rikitarwa.
Su ma kansu Misirawan a tsakanin su, sukan kasance cikin ruɗani a game da batun nahiyar da ya kamata su yi tutiya da ita a matsayin nahiyarsu. Ga su dai a cikin kwazazzabon nilu, da mediterenean, da Sahara, har ila yau kuma ga su cikin duniyar Musulmai, dukkan waɗannan siffofi, siffofi ne da kuma ba kasafai ya kamata a ce wata ƙasa guda ɗaya ta haɗa su ba. To, sai dai duk da haka za a iya cewa, mafi yawan faɗin ƙasar yana ɓangaren nahiyar Afirka ne. To, amma fa duk da haka ana kallon garuruwan da suke lardin Sinai na ƙasar Misiran a matsayin ɓangaren nahiyar Asiya, kasancewar su, suna yankin gabashin ƙasar ne.
Kogin Nilu wanda shi ne kogi mafi girma a duniya. A zamanin da can, dangantakar Misra da ƙasashen da ke Afirka na da matukar ƙarfi. To amma tun lokacin da Siriyawa da ke ƙarƙashin daular Rumawa suka mamaye Misira, a ƙarni na bakwai kafin zuwan Annabi Isa Alaihissalam, sai Misira ta fuskanta zuwa ga Yankin Gabas ta Tsakiya, ta fuskar harkokin al'adunta, da na addininta da na siyasarta da kuma na tattalin arzikinta. Kuma mafiya yawan Misirawa suna danganta kansu ne da Larabawa kuma ƴan Yankin Gabas ta Tsakiya. Har ila yau, kuma wasu da yawa daga cikinsu, kusan ace waɗanda suke su ne 'yan asalin ƙasar ta Misira, waɗanda kuma aka fi sani da Nubiyawa, suna danganta kansu ne da Afirka. Hasali ma suna iƙirarin su jinin Afirka ne.

Babu shakka dai idan aka bi salsala ta tarihi, shekaru kimanin 200 da suka gabata, Misra tana da alaƙa mai ƙarfi da ƙasashe irin su Sudan da Habasha da Libya da ma wasu ƙasashe da dama na nahiyar ta Afirka. Kuma ba tare da wani kokwanto ba, Misra za ta cigaba da cin tudu biyu, a matsayinta na ruwa-biyu, wato ga ta dai 'yar Afirka, kuma 'yar yankin Gabas ta Tsakiya, yana daga cikin tarihin Misira kasancewarta

gari na farko a tarihi da sheɗan da kansa ya bayyana ga azzalumin sarki Fir'auna a lokacin da Fir'auna ya ce shi Ubangiji ne.
Tarihi
[gyara sashe | gyara masomin]Ƙasar na da matukar tarihin gaske a yankin Afirka da duniya gabaki ɗaya.
-
Gidan tarihi da ke Cairo babban birnin ƙasar
-
Wani tsohon hoto
Al'adu
[gyara sashe | gyara masomin]Abinci
[gyara sashe | gyara masomin]-
Hatsi daga kasar Misra
Tufafi
[gyara sashe | gyara masomin]Yarika
[gyara sashe | gyara masomin]Mulki
[gyara sashe | gyara masomin]


Kasan misra tana da karfin mulki.
-
Jana'izar Hosni Mubarak
-
Hosni tare da Obama
-
Hosni Mubarak
-
Taro a kasar Misra
Sufuri
[gyara sashe | gyara masomin]
Arziki
[gyara sashe | gyara masomin]Noma
[gyara sashe | gyara masomin]Kasar Misra na da dabino da furanni daban-daban.
-
Dabino
-
Fure
-
Farin Fure
-
Fure mai launika iri iri
Kiwon lafiya
[gyara sashe | gyara masomin]Akwai asibitoci da'ake kula da marasa lafiya
-
Wasu mata sun saka takunkumin hanci Don samun kariya ga cutar "Covid 19"
Wasanni
[gyara sashe | gyara masomin]Addini
[gyara sashe | gyara masomin]Musulunci
[gyara sashe | gyara masomin]-
Masallaci a Misra
-
Haraba
Kiristanci
[gyara sashe | gyara masomin]Tsaro
[gyara sashe | gyara masomin]Hotuna
[gyara sashe | gyara masomin]-
Sabon babban birnin gudanarwa
-
Coat of Arms
-
Tutar kasar
Manazarta
[gyara sashe | gyara masomin]A wajen karshen watan da ya gabata wani mummunan lamari ya faru a bakin tekun Abu Tlat da ke yankin Al-Ajami, a yammacin birnin Iskandiriya na kasar Masar, inda dalibai mata shida da wani dalibin namiji daya suka mutu wasu kuma suka jikkata. Lamarin ya faru ne a lokacin da tawagar dalibai daga jihar Sohag a daya daga cikin makaratun koyar da aikin otal suka je wajen atisaye. Bayanai sun nuna cewa igiyar teku ce ta ja daliban yayin da masu lura da su a lokacin suka kasa yin komai su cece su. Yasser Abdul Majeed, mahaifin Fares, daya daga cikin daliban da ruwan ya ci, ya ce : ''Ina duba Facebook kawai sai na ga labarin abin da ya faru daya daga cikin abokan karatunsu ya sa labarin, daga nan sai na kira shi, inda ya gaya min cewa ai ya rasu.'' Daya daga cikin abokan Fares, wanda yana daga cikin wadanda suka tsira a hadarin na teku, Hani Rashad Abdul Aziz, ya ce: ''Sun dauke mu daga masaukinmu inda suka kai mu bakin teku da karfe takwas na safe suka ce mu shiga teku. Lokacin da muka shiga sai muka ga matan nutsewa a ruwa, dalibai da dama sun yi kokarin cetonsu. Mun nemi taimako amma ba wanda ya zo, su kuma masu lura da mu na makaranta ba wanda ya iya ruwa ko aikin ceto.''Daga bayanin da Hani ya yi, Fares ya yi kokari ya ceci 'yan mata shida kafin igiyar teku ta yi ciki da shi. Najla Hassan, mai shekara 18, daya daga cikin 'yan matan da suka tsira daga tekun ta yi bayanin yadda lamarin ya faru: "Da farko an gaya mana cewa za mu je bakin tekun ne mu dan gwada, amma ba sai mun shiga can cikin ruwan ba, to amma tuni mun shiga. Wasu daga cikin 'yan matan sun zauna a baki-baki ruwan na jan su ciki. Mun gargadi masu kula da mu a kan abin nan, amma suka ce ai yanzu za a fita. Haka ruwa ya ja su ba wanda ya iya cetonsu. Ni a haka na yi kokari na fice.[1]
Mahaifin Fares ya ce dansa yaro ne mai kokari sosai a makarantar da yake ta karatun aikin likita da jinya.Gwamnatin Iskandiriya ta ce an fara bincike kan abin da ya janyo hadarin, tare da duba matakan da aka dauka na kiyaye hadura a lokacin ziyarar daliban. Hukumar birnin ta ce bakin tekun na Ab Talat ba waje ne da ya kamata a je wanka ko wasa ba a wani lokaci saboda hadarin da ke tattare da wajen na karfin igiyar ruwa. Hukumomin birnin a karon farko tsawon lokaci sun sa an rufe wuraren wasa na bakin teku na biranen Iskandiriya da Alamein da Baltim, saboda irin ayyukan da mazauna kauyukan bakin tekun ke yi na sauya yanayin bakin ruwan wanda hakan yake sauya yanayin igiyar ruwa. Abin da hukumomi ke gargadi da a daina yi saboda akwai bukatar samun izini da shawarar kwararru a kan hakan. A lokuta da dama hukumar hasashen yanayi na fitar da sanarwa inda ake roko da jama'a da masu yawon bude idanu su yi hankali da zuwa bakin teku, saboda haukan da ruwan ke yi a wasu lokutan.[2]
Duk da yadda ake yawan samun hadarin da teku ke cin mutane, gwamnan jihar Iskandiriya Manjo Janar Ahmed Khaled, ya ce yawan hadarin ya ragu a wannan shekarar da kashi 70 cikin dari idan aka kwatanta da shekarun baya. Ya ce an samu raguwar ne sakamakon matakai da ake dauka da kuma horo da ake kara bai wa masu aikin ceto. Daga irin wadannan matakan wadanda suka shafi yaki da sauyin yanayi da gwamnatin Masar ta fara a 2019, tana kokarin samar da kariya ga mazauna yankunan bakin teku da ke kwari. Haka kuma hukumomi na samar da hanyoyin sa-ido da nazarin sauyin yawan ruwan teku da kuma yadda yake cin yankunan bakin ruwan. Wani binciken da Israa Al-Masri na Jami'ar Iskandiriya ya yi ya nuna cewa yankin gabar teku ( tsakanin Hyena da Ras al-Hikma) da ruwa ke cinyewa a duk shekara tsakanin 1990 zuwa 2020, yana da yawa. Girman ya yi yawa sosai idan aka kwatanta da wanda rahoton Bnkin Duniya ya bayar a kan yankin Gabas ta Tsakiya da Afirka ta Yamma. Rahoton ya nuna cewa gabar tekun Bahar Rum ta Masar na rasa kusan kafa digo uku (0.328084 ko 10cm), inda ruwa ke cinyewa a duk shekara tsakanin 1984 da 2016. Shugaban majalisar tabbatar da ayyukan raya kasa na Masar, Imad El-Din Adly, ya yi nuni da cewa sauyin yanayi da karuwar ruwan teku da ake dangantawa da dumamar yanayi, da yawan ruwan sama da sauyin yanayin zafi da sanyi da ake gani sosai, duka wadannan na janyo sauyi a yanayin bakin teku. Haka kuma duka wadannan abubuwan da sa ruwa ya cinye yankunan da ke gaba cikin sauri, wanda kuma ba a ganin hakan a da, a cewar shugaban.[3]
Jami'in na ganin rashin wayar da kan masu yawon bude idanu ya kara hadarin mutuwa a ruwa, musamman ma idan ba su kiyaye da gargadin masu kula da bakin tekun ba. Ta yaya za mu yi maganin fushin teku?[4]
Kwararre a kan harkar teku Sabri Al-Jundi ya gabatar da wasu shawarwari ta yadda za a kiyaye hadari tare da kare lafiyar masu yawon bude idanu a bakin teku, kamar hakan:[5]
1- A rika bayar da horo lokaci zuwa lokaci ga dukkanin masu ninkaya[6]
2- Samar da kayayyaki na zamani na aikin ceto
3 - Kada a dogara ga masu nutso ko ninkaya mutane kadai[7]
4- A tabbatar da cewa mutane na bin dokokin hukuma da ke kula da bakin tekun[8]
5- Kada a je bakin teku ranar da igiyar ruwa ke da karfi ( teku ke hauka)[9]
6- Ma'aikatar kula da albarkatun ruwa ta rika nazai tare da bayyana wa jama'a wuraren bakin teku da ke da hadari.[10]
7- A sanya abubuwan da za su hana mutane shiga wurin da ke da hadari.[11]
| Ƙasashen Afirka |
| Afirka ta Tsakiya | Aljeriya | Angola | Benin | Botswana | Burkina Faso | Burundi | Cabo Verde | Cadi | Côte d'Ivoire | Eritrea | eSwatini | Ethiopia | Gabon | Gambiya | Ghana | Gine | Gine Bisau | Ginen Ekweita | Jibuti | Kameru | Kenya | Komoros | Kwango (JK) | Kwango (JDK) | Laberiya | Lesotho | Libya | Madagaskar | Mali | Moris | Muritaniya | Misra | Morocco | Mozambik | Namibiya | Nijar | Nijeriya | Ruwanda | Saliyo | Sao Tome da Prinsipe | Senegal | Seychelles | Somaliya | Sudan | Sudan ta Kudu | Tanzaniya | Togo | Tunisiya | Uganda | Zambiya | Zimbabwe |
