Bayelsa

Daga Wikipedia, Insakulofidiya ta kyauta.
(an turo daga Jihar Bayelsa)
Bayelsa
Bayelsa State (en)


Wuri
Map
 5°N 6°E / 5°N 6°E / 5; 6
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya

Babban birni Yenagoa
Yawan mutane
Faɗi 2,277,961 (2016)
• Yawan mutane 107.91 mazaunan/km²
Harshen gwamnati Turanci
Labarin ƙasa
Yawan fili 21,110 km²
Sun raba iyaka da
Bayanan tarihi
Mabiyi Jihar rivers
Ƙirƙira 1 Oktoba 1996
Tsarin Siyasa
Majalisar zartarwa Executive Council of Bayelsa State (en) Fassara
Gangar majalisa Bayelsa State House of Assembly (en) Fassara
Bayanan Tuntuɓa
Kasancewa a yanki na lokaci
Lamba ta ISO 3166-2 NG-BY
Lambar Bayelsa
al'ummar Bayelsa
Cikin kasuwar Swali a birnin Bayelsa
Kogin bayelsa
Daya daga cikin cocin jahar bayelsa
Al adon balyalsa

Jihar Bayelsa jiha ce dake kudu maso kudancin Najeriya, tana nan a tsakiyar yankin Niger Delta.[1][2] An kirkiri Jihar Bayelsa[3] ne a shekara ta alif dubu daya dari Tara da casa'in da shida (1996), kuma an cire ta ne daga Jihar Rivers.[4] Hakan yasa ta zamo daya daga cikin sabbin jihohin kasar. Ta hada iyaka da Jihar Rivers[5] daga gabas, da kuma Jihar Delta daga yamma, inda tekun Tekun Atalanta[6] ta mamaye yankin kudancin jihar.[2]

Jihar Bayelsa da fadin fili na kimani na kilomita 10,773kmaq, wanda yasa ta zamo jiha mafi karancin fili a Najeriya.[7] Kuma tana da yawan jama’a kimanin mutum 2,394,725 (ƙiyasin shekara ta 2016), wanda ya sanya ta jiha mai mafi karancin mutane. Babban birnin jihar, itace Yenagoa. Douye Diri ne gwamnan jihar a shekara ta 2022, mataimakin shi kuma shine Lawrence Ewhrudjakpo.[8] Dattijan jihar sun hada da: Goodluck Jonathan, David Clark, Ben Murray Bruce, Emmanuel Paulker Izibefien da Evan Foster Ogola. A sanadiyyar kasancewarta a yankin Niger Delta, Jihar Bayelsa mamaye take da kogi da koramu, kuma kusan duka garin cikin ruwa yake, hakan ya jawo rashin cigaba ta hanyar gina hanyoyi.[9]

Ana amfani da harshen Ijaw a ko ina a jihar, tare da sauran harsuna kamar Isoko da Urhobo a tsaffin kyaukan jihar.

Bukukuwan bayelsa

Tana da kanan hukumomi 8: Ekeremor, Kolokuma/Opokuma, Yenagoa, Nembe, Ogbia, Sagbama, hi Brass da kuma Ijaw kudu. Bayelsa ta kasance gida ga Mutanen Urhobo a karamar hukumar Sagbama.[10]

A dalilin kasancewarta a yanki mai arkin man-fetur wato Niger Delta, tattalin arzikin Jihar Bayelsa sun ta'allaka ne akan aka man-fetur da ma'aikatun tace su. Yankin Oloibiri Oilfield inda aka fara hako man fetur a Najeriya.[11] Sannan zuwa shekara ta 2015, an kiyasta cewa tana samar da kusan kashi 30-40% na man fetur din Najeriya.[12] Ana yiwa jihar lakabi da “Glory of all Lands” sannan ita ke da tafkin gas mafi girma a Najeriya (18 trillion cubic feet).[13] Duk da cewa jihar ta mallaki manyan rijiyoyin mai kuma tana taka muhimmiyar rawa wajen cigaban tattalin arzikin kasa, talauci yayi wa jihar katutu, hadi da gurbacewar muhalli[14] daga fesowar man fetur.[15][16]

Siyasa[gyara sashe | gyara masomin]

Ya zuwa shekara ta 2022, zuwa shekara ta 2022 Douye Diri ne gwamnan jihar, a yayinda Lawrence Ewhrudjakpo ke matsayin mataimakinshi.[17]

Kananan Hukumomi[gyara sashe | gyara masomin]

Jihar Bayelsa nada Kananan hukumomi guda takwas, Sune:

  1. Brass
  2. Ekeremor
  3. Kolokuma/Opokuma
  4. Nembe
  5. Ogbia
  6. Sagbama
  7. Southern Ijaw
  8. Yenagoa

Wuri[gyara sashe | gyara masomin]

Bayelsa na daga cikin jihohin kudancin Najeriya, jihar na nan a tsakiyar yanki Niger Delta. An cire Jihar Bayelsa daga Jihar Rivers, kuma tana daga cikin sabbin jihohin Najeriya.[18]

Jihar Bayelsa ta hada iyaka da Jihar Rivers daga gabas, Jihar Delta (jiha) daga yamma, a yayin da ruwan Tekun Atalanta ya mamaye yankin kudancin Jihar.[19]

Tarihi[gyara sashe | gyara masomin]

A karni na 20th, bukata na samar da sabuwar jiha da harshen Ijaw ke da rinjaye a yankin Niger Delta ya zamo sanannen abu. A tsakanin shekara ta 1941 zuwa ta 1956, an kafa kungiyoyi da dama dake goyon bayan samar da jiha na Mutanen Ijaw a yankin Kudancin Najeriya. Isaac Adaka Boro, wani shahararren dan gwagwarmayar Ijaw a shekara ta 1960 wanda aka haifa a Oloibiri yayi yinkurin ikirarin "Jimhoriyar Mutanen Niger Delta ("Niger Delta Peoples Republic") a shekara ta 1966.[20][21][22] Shugaban kasa na mulkin mallaka ya Sani Abacha ne ya kirkiri Jihar Bayelsa daga Jihar Rivers a ranar 1 ga watan Oktoban, shekara ta 1966.[23] An samo asalin sunan ne daga haruffan farko na sunayen kananan hukumomin ta: Brass LGA (BALGA), Yenagoa LGA (YELGA) da kuma Sagbama LGA (SALGA).[19]

A ranar 20 ga watan Disamban shekara ta 1999 ne sojojin Najeriya suka kaddamar da abinda aka fi sani da Kisan Kiyashin Odi. Ana kokanta akan ainihin yawan mutanen da aka kashe, duk da cewa, Nnimmo Bassey, Babban Darekta na Hakkin Harkokin Muhalli, ya sanar cewa farar hula mutum 2500 ne suka rasa rayukansu.[24][25]

Dangane da zaizayar kasa a jihar a dalilin ma'aikatun man fetur, anyi zanga-zanga da dama kamar "Rise for Bayelsa" da akayi don inganta samar da ruwan sha a kananan yankuna. A cikin shekara ta 2019 ne, gwamnatin jihar Bayelsa ta fara neman gwagwarmayar samar da mafita dangane da matsalolin gurbacewar muhalli a jihar.[26][27]

Tattalin arziki[gyara sashe | gyara masomin]

Jihar na daya daga cikin jiha mafi albarkatun man fetur a Najeriya.[28][29] A dalilin haka, akwai yawaitar man fetur a jihar. Duk da cewa jihar tana da arziki mai, jihar na samun karancin kudi daga kasafin man fetur a dalilin rashin daidaituwa a tsarin kasafi daga gwamnatin kasar.[30]

Yanayin kasa[gyara sashe | gyara masomin]

Bayelsa na zagaye da ruwan kogi da kuma koramu. Yankunan jihar da dama suna kewaye ne da ruwa wanda haka yasa ba iya riskar su ta tituna. Akwai gandun daji na "Edumanom Forest Reserve" a jihar. Tun watan Yunin shekara ta 2008, inda aka ga birin chimpanzee na karshe itace Niger Delta.[31] Sauran muhimman birane bayan Yenagoa sun hada da; Akassa, Lobia, Amassoma (the home of the Niger Delta University), Eniwari, Ekeremor, Aliebiri, Peretoru, Twon-Brass, Egwema-Brass, Kaiama, Nembe, Odi, Ogbia, Okpoama, Brass, Oporoma, Korokorosei, Otuan, Koroama, Okolobiri, Obunagha, Ogboloma, Sagbama, Olugbobiri, Peremabiri, Ekowe, da kuma Swali.

Akwai kuma ginin Akassa Lighthouse wanda ke nan tun shekara ta 1910.[32]

Harsuna[gyara sashe | gyara masomin]

Asalin harshen da ake amfani dashi shin harshen Ijaw, tare da yaruka kaman Kolukuma, Mein, Bomu, Nembe, Epie-Atisa, da kuma Ogbia. Kamar dai a sauran jihohin Najeriya, Turanci ne harshen gwamnatin jihar.

Jerin harsunan Jihar Bayelsa dangane da kananan hukumomin LGA da ake amfani dasu:[33]

Ekeremor, Bayelsa State
LGA Languages
Brass Abureni; Southeast Ijo; Ogbia; Kugbo
Ekeremor Izon
Kolokuma Opokuma Izon
Nembe Abureni; Southeast Ijo. Izon (Ijaw)
Ogbia Abureni; Southeast Ijo; Odual; Ogbia; Oruma
Sagbama Biseni; Isoko; Izon; Ogbah; Okodia; Urhobo
Ijaw ta Kudu Southeast Ijo; Izon
Yenagoa Engenni; Epie; Izon; Ekpeye

Matsaloli na muhalli[gyara sashe | gyara masomin]

Gurbacewar iska[gyara sashe | gyara masomin]

Wannan wani bakin hayaki ne da ke tashi a dalilin kona man fetur ba tare da ka'ida ba (ana kiransu a gargajiyance "wutan Kpo).[34] Wadannan mugayen sinadirai kan jawo rashin lafiya kamar Ciwon huhu na daji, matsalolin fata, matsala ta mashakar iska da dai sauransu. Ana iya ganin sauran illolinta kamar gurbacewar iska, ruwa da kasa wanda hakan sun jawo mutuwan tsirrrai, mutane da kuma dabbobi.[35]

Ambaliya[gyara sashe | gyara masomin]

Wannan sanannen matsala ne a Jihar Bayelsa saboda tana kan gabar Tekun Atalanta. Hauhawar igiyar ruwan teku ne muhimmin dalili na ambaliyar. Ambaliyar ta haifar da matsaloli ga al'ummomi da dama, dukiyoyi da kuma mutane. Kusan ko ina a Bayelsa na fuskantar matsalolin ambaliya, amma ambaliyar tafi tasiri a yankuna kamar Ekeremor, Ijaw ta kudu, Sagbama, Kolokuma/Opokuma da kuma Yenagoa wanda suke fuskantar barazanar duk shekara.[36] Rashin bin tsarin gine-gine na daga cikin dalilan dake assasa ambaliya a Jihar Bayelsa.[37]

Zubewar mai[gyara sashe | gyara masomin]

Wannan wani muhimmin al'amari ne dake kawo matsalar muhalli a Jihar Bayelsa a dalilin ayyukan kamfanonin man fetur a jihar. Zubewar mai na jwo illa ga gonaki, halittun ruwa da kuma mutane.[38] Kusan duk rana ana sanarwa Udengs Eradiri labarin zubar mai a Jihar Bayelsa, Niger Delta.

Kamar yadda yake fadi, a da zaki iya yin noma ka samu girbi mai kyau, ko kuma kaje kamun kifi ka kamo da yawa, amma yanzu zaka iya kwashe tsawon yini baka kama kifi ko guda ba.[39]

Wata matsala ta muhalli itace gurbacewar iska (Soot), wanda mafi akasarin mutanen Bayelsa na kukan cewa basu iya numfashi da kyau.[40]

Amma a shekara ta 2018, masu hanu da shuni sunyi kamfe mai taken "Save Rivers from this soot of death" wato a kiyaye koguna daga mutuwar Soot, a yankunan dake kewaye da ruwa.[41]

Ilimi[gyara sashe | gyara masomin]

Jihar Bayelsa nada makartu mataki daban daban wanda ke bayar da ilimi ga daukacin al'ummar jihar

Jami'o'i[gyara sashe | gyara masomin]

Makarantun gaba da sakandare a bayelsa sun hada da

  • Jami'ar Neja Delta
  • College of Health Science Bayelsa
  • Isaac Jasper Boro College of Education
  • College of Nursing Bayelsa
  • Bayelsa Medical University
  • Bayelsa State College of Art and Science
  • University of Africa
  • International Institute of Tourism and Hospitality[42]

Sanannun Mutane[gyara sashe | gyara masomin]


Manazarta[gyara sashe | gyara masomin]

  1. "Yenagoa | Location, Facts, & Population". Encyclopedia Britannica. Retrieved 2021-09-11.
  2. 2.0 2.1 "Bayelsa – History & Culture – Bayelsa State Government". Retrieved 2021-09-11.
  3. "Bayelsa State". BBC News Pidgin. Retrieved 2022-03-06.
  4. "Rivers state Archives". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News. Retrieved 2022-03-06.
  5. "Rivers state Archives". The Guardian Nigeria News - Nigeria and World News. Retrieved 2022-03-06.
  6. "The Atlantic Ocean—facts and information". Environment. 2019-03-18. Retrieved 2022-03-05.
  7. "Central Bank of Nigeria | Home". www.cbn.gov.ng. Retrieved 2022-03-09.
  8. "Governor Diri, Odi School alumni raise funds for science laboratory project". Tribune Online. 2022-03-16. Retrieved 2022-03-23.
  9. "Bayelsa". Nigeria. 2020-09-15. Retrieved 2021-09-10.
  10. "Our Story". Indigenous People of Biafra USA. Retrieved 2021-03-07.
  11. "Industry History". nnpcgroup.com. Retrieved 2021-03-09.
  12. "Conflict Bulletin: Bayelsa State – Patterns and Trends, 2012-2014 | The Fund for Peace". fundforpeace.org. Retrieved 2021-03-09.
  13. "Bayelsa State". Nigerian Investment Promotion Commission. 2019-01-07. Retrieved 2021-09-11.
  14. "pollution | Definition, History, Types, & Facts | Britannica". www.britannica.com. Retrieved 2022-03-09.
  15. "Nigeria's oil-rich Bayelsa State opens inquiry on spills". www.worldoil.com. Retrieved 2021-03-07.
  16. "'This place used to be green': the brutal impact of oil in the Niger Delta". the Guardian. 2019-12-06. Retrieved 2021-03-07.
  17. "Governor Diri, Odi School alumni raise funds for science laboratory project". Tribune Online. 2022-03-16. Retrieved 2022-03-23.
  18. "Référence rapide des codes de la CITE-P et de la CITE-A dans la CITE 2011", Guide opérationnel CITE 2011, OECD, pp. 117–118, 2016-01-25, doi:10.1787/9789264248823-16-fr, ISBN 9789264248830, retrieved 2021-09-10
  19. 19.0 19.1 "Learn About Bayelsa State, Nigeria | People, Local Government and Business Opportunities in Bayelsa". Overview of Nigeria |NgEX. Retrieved 2018-07-29.
  20. T., Akinyele, R. (2006). Isaac Adaka Boro : patriarch of minority activism in the Niger Delta. University of Lagos, Faculty of Arts. ISBN 978-075-054-1. OCLC 752210539.
  21. "Overview of Bayelsa State". Niger Delta Budget Monitoring Group. Retrieved 2021-03-09.
  22. Organ., Thomson Reuters Herausgebendes. Social sciences citation index. OCLC 946102050.
  23. "Bayelsa – History & Culture – Bayelsa State Government". Retrieved 2022-02-11.
  24. "Trade and human rights in the Niger Delta | Pambazuka News". www.pambazuka.org. Retrieved 2021-03-09.
  25. "Odi massacre: Anyone with tribal marks on their chest was slaughtered, corpses littered everywhere –Bolou, former Bayelsa commissioner". Punch Newspapers. 2017-12-16. Retrieved 2021-09-10.
  26. "Nigeria: Bayelsa state launches new inquiry into the environmental and human damage caused by oil spills in the Niger Delta". Business & Human Rights Resource Centre. Retrieved 2021-09-10.
  27. "Nigeria's oil-rich Bayelsa State opens inquiry on spills". www.worldoil.com. Retrieved 2021-03-09.
  28. "Bayelsa woos oil, gas, other investors". Vanguard News. 2019-04-23. Retrieved 2021-09-17.
  29. "Bayelsa woos oil, gas, other investors". Vanguard News. 2019-04-23. Retrieved 2021-09-11.
  30. Ikein, Augustine (2004). "Economic Development Agenda for Bayelsa State of Nigeria: An Advisor's Opinion" (PDF). Journal of Sustainable Development in Africa. Archived (PDF) from the original on 2009-01-07.
  31. "Nigeria Biodiversity and Tropical Forestry Assessment" (PDF). USAID. June 2008. p. 76. Retrieved 2010-09-18.
  32. "Since 1910, a Lighthouse in the Creeks". Folio Nigeria. Retrieved 17 August 2020.
  33. "Nigeria". Ethnologue (22 ed.). Retrieved 2020-01-10.
  34. "Soot pollution in Rivers, Bayelsa: All hands must be on deck". Vanguard News. 2022-01-05. Retrieved 2022-03-25.
  35. "Anxiety as strange black soot envelops Yenagoa". Vanguard News. 2021-12-28. Retrieved 2022-04-01.
  36. "Diri faults NEMA's report, insists entire Bayelsa is flood prone". Vanguard News. 2020-09-09. Retrieved 2022-04-04.
  37. News Express. "Environmentalists identify cause of flooding in Yenagoa". News Express.
  38. "Oil spill: We can't breathe, we're dying of hunger — Bayelsa communities lament". Vanguard News. 2021-11-27. Retrieved 2022-03-25.
  39. "'This place used to be green': the brutal impact of oil in the Niger Delta". the Guardian. 2019-12-06. Retrieved 2022-03-25.
  40. "Soot pollution in Rivers, Bayelsa: All hands must be on deck". Vanguard News. 2022-01-05. Retrieved 2022-03-25.
  41. "'This place used to be green': the brutal impact of oil in the Niger Delta". the Guardian. 2019-12-06. Retrieved 2022-03-25.
  42. https://independent.ng/bayelsa-govt-tasks-governing-councils-of-state-owned-tertiary-institutions/amp/
  43. "Diezani Alison-Madueke scored another firs - Vanguard News". Vanguard News (in Turanci). 2014-12-02. Retrieved 2018-07-30.
  44. "Noah Bazee biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2021-09-12.
  45. "Who Killed Adaka Boro". www.gamji.com. Retrieved 2018-07-30.
  46. "TIMI DAKOLO". PraiseMaMa.com (in Turanci). Archived from the original on 2018-07-30. Retrieved 2018-07-30.
  47. "Edmund Daukoru". www.gamji.com. Retrieved 2018-07-30.
  48. Society, Urhobo Historical. "Former Military Governor Diete-Spiff Reflects On Background Problems of the Invasion". www.waado.org. Archived from the original on 2018-02-19. Retrieved 2018-07-30.
  49. "Hon. Douye Diri biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2021-09-12.
  50. "Tamara Eteimo biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2021-09-12.
  51. "ETETE, Chief Dan Lauzia". Biographical Legacy and Research Foundation (in Turanci). 2017-02-03. Retrieved 2018-07-30.
  52. "Nigeria: Eagles, Black Stars Will Survive Group Stage -Finidi". This Day (Lagos). 2010-03-24. Retrieved 2018-07-30.
  53. "DANIEL IGALI - From obscurity to wrestling stardom - The Nation Nigeria". The Nation Nigeria (in Turanci). 2016-07-03. Retrieved 2018-07-30.
  54. "Unsung heroes of independence - The Nation Nigeria". The Nation Nigeria (in Turanci). 2015-10-02. Retrieved 2018-07-30.
  55. "Biography | The Office of Goodluck Ebele Jonathan". www.gej.ng (in Turanci). Archived from the original on 2018-07-30. Retrieved 2018-07-30.
  56. Falae, Vivian. "Present Nigerian Ministers and their portfolios". legit.ng.
  57. "Ben Murray-Bruce biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2021-09-12.
  58. Egba, Abdullahi (3 June 2021). "Ogborodi Appointed Acting NECO Registrar After Obioma's Death". Channels TV. Retrieved 3 June 2021.
  59. "Gabriel Okara | Nigerian author". Encyclopedia Britannica (in Turanci). Retrieved 2018-07-30.
  60. "How Governor Melford Okilo Discovered Olumba Olumba Brotherhood - Brand Campaign". Brand Campaign (in Turanci). 2016-09-14. Archived from the original on 2018-07-30. Retrieved 2018-07-30.
  61. "Ebinabo Potts-Johnson biography, net worth, age, family, contact & picture". www.manpower.com.ng. Retrieved 2021-09-12.
  62. "Bayelsa honours Samson SIasia, others". Premium Times Nigeria (in Turanci). 2018-05-18. Retrieved 2018-07-30.
  63. "Masquerades and Jokers as Governors in Bayelsa State". www.gamji.com. Retrieved 2018-07-30.
  64. "Afrotainment-Museke Online African Music Awards 2011". 3-mob.com. 2011-09-28.



Jihohin Najeriya
Babban birnin tarayyar (Abuja) | Abiya | Adamawa | Akwa Ibom | Anambra | Bauchi | Bayelsa | Benue | Borno | Cross River | Delta | Ebonyi | Edo | Ekiti | Enugu | Gombe | Imo | Jigawa

Kaduna | Kano | Katsina | Kebbi | Kogi | Kwara | Lagos | Nasarawa | Neja | Ogun | Ondo | Osun | Oyo | Plateau | Rivers | Sokoto | Taraba | Yobe | Zamfara